Gwamnatin jihar Katsina Da Optimal Image Ta Shirya Taron Horaswa Ga Ma’aikatan Yaɗa Labarai Na Gwamna

top-news

Gwamnatin Jihar Katsina, tare da haɗin gwiwar kamfanin Optimal Image Media Limited, ta shirya taron horaswa na kwanaki biyu domin inganta ƙwarewar jami'an watsa labarai da kuma mataimakan gwamna kan kafafen sada zumunta daga ƙananan hukumomi 34 na jihar. An gudanar da taron ne a Hukumar Kula da Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi ta Jihar Katsina, tare da nufin ba wa mahalarta horon da ya dace don yakar yaduwar labaran ƙarya, musamman dangane da matsalar tsaro da ake fama da ita a jihar da yankin arewa baki ɗaya.

A jawabin maraba da ya gabatar, Manajan Daraktan Optimal Image Media Limited, Dahiru Hassan Kera, ya jaddada muhimmancin isar da sahihan bayanai, musamman duba da halin rashin tsaro da jihar Katsina ke ciki. Ya nuna cewa wannan horon yana da matuƙar muhimmanci wajen ba 'yan jarida da masu amfani da kafafen sada zumunta horo don sarrafa kafafen yada labarai cikin natsuwa da inganta manufofin gwamnati.

Dokta Sha’aubu Mungadi, Shugaban Majalisar Gudanarwa ta Optimal Image Media Limited, ya yaba wa Gwamnatin Jihar Katsina, karkashin jagorancin Gwamna Dikko Umar Radda, bisa fahimtar muhimmancin kafafen sada zumunta na zamani. Ya bayyana cewa, wannan taron na cikin wani shiri ne na haɗin gwiwa tsakanin gwamnati da kamfanin Optimal Image Media Limited don inganta ƙwarewar ma'aikatan watsa labarai wajen isar da manufofin gwamnati da kuma ƙarfafa gaskiya a mulki.

Da yake wakiltar Kwamishinan yada labarai na jihar Katsina, Amadi Abubakar Balarabe, babban Sakatare a Ma’aikatar yada labarai da al'amuran cikin gida na Jihar, ya sake jaddada aniyar gwamnati na tabbatar da cewa jami’an yada labarai da mataimakan gwamna kan kafafen sada zumunta zasu samu ingantaccen horo da ya dace don zama wata gada tsakanin gwamnati da al’umma. Ya yi nuni da cewa, muhimmancin wannan taron shi ne inganta ƙwarewar mahalarta wajen isar da sahihan bayanai da tattara muhimman ra’ayoyi daga talakawa.

Taron horaswar, mai taken "Isar da Manufofi da Aiwatar da Su: Rawar Da Kafofin Watsa Labarai Ke Takawa," ya nuna yadda mahalarta taron ke nuna godiyarsu bisa wannan dama ta inganta ƙwarewarsu da fahimtar muhimmiyar rawar da suke takawa wajen tsara tunanin jama'a da kuma tallafa wa gwamnatin jihar Katsina.

NNPC Advert